Dan majalisar wakilan Nijeriya mai wakiltar Apa/Agatu da ke jihar Benue, Ojoma Ojotu ya fice daga jam’iyyar PDP tare da komawa APC.
Bayanin sauya shekar dan majalisar na kunshe ne cikin wasikar da mataimakin kakakin majalisar Benjamin Kalu ya karanto yayin zaman zauren na ranar Talata, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Da wannan ficewa ta dan majalisa Ojotu, jam’iyyar APC ta mamaye dukkanin kujerun wakilcin jihar ta Benue a zauren majalisar ta wakilan Nijeriya.



