DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dattawan Nijeriya ta bukaci gwamnati ta kara wa sojoji albashi

-

Majalisar dattawan Nijeriya ta bukaci gwamnati ta sake yin duba kan albashin da ake biyan jami’an tsaro musamman ma soji a fadin kasar.

Majalisar ta bayyana cewa dalilin wannan kira shi ne ta damu matuka da yadda ake fama matsin tattalin arziki baya ga tsadar rayuwa.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito cewa kiran ya biyo bayan kudirin da Sanata mai wakiltar Borno ta kudu kuma tsohon bulaliyar majalisar Ali Ndume ya gabatar a zamanta na yau Talata.

A cewar Ndume, duba da yadda jami’an tsaron Nijeriya ke sadaukar da rayukansu wajen kare ‘yan kasa, akwai bukatar a inganta albashi har ma da walwalar su.

Ya kuma kara da yin tuni ga majalisar cewa sojoji a wasu kasashen Afirka da dama na samun albashi fiye da na Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan Bauchi ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar

Gwamnan Bauchi Bala Muhammad ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar. Daily Trust ta ruwaito cewa a lokacin da yake sanya...

Kenya da Senegal sun kulla yarjejeniyar shige da fice ba tare da biza ba

Gwamnatocin Kenya da Senegal sun bai wa juna damar shige da fice ga 'yan kasashensu ba tare da biza ba na tsawon kwanaki 90. DW Africa...

Mafi Shahara