DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dattawan Nijeriya ta bukaci gwamnati ta kara wa sojoji albashi

-

Majalisar dattawan Nijeriya ta bukaci gwamnati ta sake yin duba kan albashin da ake biyan jami’an tsaro musamman ma soji a fadin kasar.

Majalisar ta bayyana cewa dalilin wannan kira shi ne ta damu matuka da yadda ake fama matsin tattalin arziki baya ga tsadar rayuwa.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito cewa kiran ya biyo bayan kudirin da Sanata mai wakiltar Borno ta kudu kuma tsohon bulaliyar majalisar Ali Ndume ya gabatar a zamanta na yau Talata.

A cewar Ndume, duba da yadda jami’an tsaron Nijeriya ke sadaukar da rayukansu wajen kare ‘yan kasa, akwai bukatar a inganta albashi har ma da walwalar su.

Ya kuma kara da yin tuni ga majalisar cewa sojoji a wasu kasashen Afirka da dama na samun albashi fiye da na Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara