DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Abin murna ne yadda al’ummar Katsina suka tarbi Kashim Shettima – Gwamna Radda

-

Gwamnan Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya gode wa al’ummar jihar bisa irin tarbar da suka yi wa mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima, yayin ziyarar kwanaki biyu da ya kai jihar.

 

Google search engine

Radda ya ce wannan goyon baya da jama’a suka nuna ba sabon abu ba ne, domin tun farkon tafiyarsa a siyasa suna tare da shi, lamarin da ke kara masa kwarin guiwar gudanar da ingantaccen mulki.

 

Gwamnan ya kuma ce duk nasarorin da gwamnatinsa ke samu, baiwa ce daga Allah tare da goyon bayan tawagarsa da kuma amincewar jama’ar jihar.

 

Ya kara da cewa hakan shi ne ginshikin sauye-sauyen da ake gani a fadin jihar Katsina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara