DCL Hausa Radio
Kaitsaye

DCL Hausa ta buɗe damar neman aiki ga Video Editor a Katsina

-

Kafar yaɗa labarai ta DCL Hausa ta sanar da buɗewar damar neman aiki ga masu ƙwarewa a fannin gyaran bidiyo (Video Editing) domin cike gurbin ma’aikaci a ofishinta na jihar Katsina.

A cikin sanarwar da ta fitar, DCL Hausa ta bayyana cewa ana buƙatar mai kwarewa a aikin gyaran bidiyo wanda zai taimaka wajen gyara rahotanni, labarai, da bidiyoyin sada zumunta, tare da tabbatar da ingancin hoto da sauti.

Google search engine

DCL Hausa ta buɗe ƙofa ga mai kwarewa a aikin gyaran bidiyo wanda ke da hangen nesa, da sha’awar samar da ingantaccen bidiyo ga masu kallonmu.

Abubuwan da ake bukata (Requirements):

  • Mazauni jihar Katsina.
  • Mai Ƙwarewa wajen gyaran bidiyo.
  • Iya amfani da Adobe Premiere Pro da Canva – kwarewa da sauran software irin su CapCut ƙarin fa’ida ne.
  • Kwarewa wajen haɗa rahotanni, labarai, da bidiyoyin sada zumunta.
  • Fahimtar dabarun haɗa sauti da hoto don samar da ingantaccen bidiyo.
  • Iya aiki cikin lokaci da bin tsarin aiki da aka gindaya.
  • Sha’awar kirkira da fasaha a fagen yada labarai.
  • Ƙwarewa wajen aiki tare da sauran ma’aikata (teamwork) da kyakkyawar mu’amala.
  • Mata za su iya neman wannan gurbin!

Cike bayananka/ki nan: https://forms.gle/EJnCwJhdM2nHY8vs9

Ana sa ran wanda ya yi nasara zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Nuwamba, 2025.

Za a kulle kofa karɓar bayanai a ranar Lahadi, 26 ga Oktoba, 2025.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon Minista Tanimu Turaki ya zama ɗan takarar shugabancin jam’iyyar PDP na Arewa

Jagororin jam’iyyar PDP na yankin Arewacin Nijeriya sun amince da tsohon Ministan Harkoki. A Musamman, Tanimu Turaki (SAN), a matsayin ɗan takarar da suka amince...

Jam’iyyar ADC a Kaduna ta kori mataimakin shugabanta da wasu ‘ya’yanta 8

Jam'iyyar hadaka ta ADC mai hamayya a Nijeriya reshen Kaduna ta kori mataimakin shugabanta na jihar tare da wasu manyan jami'anta guda takwas, bayan samun...

Mafi Shahara