DCL Hausa Radio
Kaitsaye

DCL Hausa ta buɗe damar neman aiki ga Video Editor a Katsina

-

Kafar yaɗa labarai ta DCL Hausa ta sanar da buɗewar damar neman aiki ga masu ƙwarewa a fannin gyaran bidiyo (Video Editing) domin cike gurbin ma’aikaci a ofishinta na jihar Katsina.

A cikin sanarwar da ta fitar, DCL Hausa ta bayyana cewa ana buƙatar mai kwarewa a aikin gyaran bidiyo wanda zai taimaka wajen gyara rahotanni, labarai, da bidiyoyin sada zumunta, tare da tabbatar da ingancin hoto da sauti.

Google search engine

DCL Hausa ta buɗe ƙofa ga mai kwarewa a aikin gyaran bidiyo wanda ke da hangen nesa, da sha’awar samar da ingantaccen bidiyo ga masu kallonmu.

Abubuwan da ake bukata (Requirements):

  • Mazauni jihar Katsina.
  • Mai Ƙwarewa wajen gyaran bidiyo.
  • Iya amfani da Adobe Premiere Pro da Canva – kwarewa da sauran software irin su CapCut ƙarin fa’ida ne.
  • Kwarewa wajen haɗa rahotanni, labarai, da bidiyoyin sada zumunta.
  • Fahimtar dabarun haɗa sauti da hoto don samar da ingantaccen bidiyo.
  • Iya aiki cikin lokaci da bin tsarin aiki da aka gindaya.
  • Sha’awar kirkira da fasaha a fagen yada labarai.
  • Ƙwarewa wajen aiki tare da sauran ma’aikata (teamwork) da kyakkyawar mu’amala.
  • Mata za su iya neman wannan gurbin!

Cike bayananka/ki nan: https://forms.gle/EJnCwJhdM2nHY8vs9

Ana sa ran wanda ya yi nasara zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Nuwamba, 2025.

Za a kulle kofa karɓar bayanai a ranar Lahadi, 26 ga Oktoba, 2025.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara