DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar NEMA ta karbi ‘yan Nijeriya 147 da suka makale a Libya

-

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta bayyana karbar ‘yan kasar 147 da suka makale a Libya.

Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X, ta bayyana cewa dawo da ‘yan kasar wani bangare ne na shirin mayar da mutane ainahin kasashensu, na hadin gwiwa tsakanin majalisar dinkin duniya da kuma gwamnati.

Google search engine

Labari mai alaka: Hukumomi a Nijeriya sun karbi ‘yan kasar 139 daga jamhuriyar Nijar

Mutanen da hukumar ta karba sun hadar da manyan maza da mata guda 100, sai yara maza da mata 34, sannan jarirai guda 13.

Tuni dai NEMA ta bayyana cewa an fara shirin daukar bayanan su ta hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya, kafin mayar da su cikin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

FIFA ta sanya $60 a matsayin kudin tikitin kallon kofin duniya na 2026

Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta ƙaddamar da sabon rukuni na tikiti a dalar Amurka 60 ga kowane ɗayan wasannin 104 na Gasar Kofin...

Likitoci sun tsunduma yajin aiki a Ingila

Ƙungiyar British Medical Association (BMA) ta tabbatar da ci gaba da gudanar da yajin aiki, bayan kashi 83 cikin ɗari na mambobinta sun amince da...

Mafi Shahara