DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar NEMA ta karbi ‘yan Nijeriya 147 da suka makale a Libya

-

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta bayyana karbar ‘yan kasar 147 da suka makale a Libya.

Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X, ta bayyana cewa dawo da ‘yan kasar wani bangare ne na shirin mayar da mutane ainahin kasashensu, na hadin gwiwa tsakanin majalisar dinkin duniya da kuma gwamnati.

Google search engine

Labari mai alaka: Hukumomi a Nijeriya sun karbi ‘yan kasar 139 daga jamhuriyar Nijar

Mutanen da hukumar ta karba sun hadar da manyan maza da mata guda 100, sai yara maza da mata 34, sannan jarirai guda 13.

Tuni dai NEMA ta bayyana cewa an fara shirin daukar bayanan su ta hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya, kafin mayar da su cikin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara