DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar ADC a Kaduna ta kori mataimakin shugabanta da wasu ‘ya’yanta 8

-

Jam’iyyar hadaka ta ADC mai hamayya a Nijeriya reshen Kaduna ta kori mataimakin shugabanta na jihar tare da wasu manyan jami’anta guda takwas, bayan samun su da aikata laifukan da suka saba wa dokokinta.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa yayin wani taron manema labarai a Kaduna, shugaban jam’iyyar na jihar Elder Patrick Ambut, ya ce korar mutanen ya zama wajibi ne kasancewar ba za ta lamunci duk abin da zai kawo hargitsi ko zubar mata da kima ba.

Google search engine

Jam’iyyar ta zargi wadanda ta kora da aikata laifukan gudanar ta tarukan sirri don shirya manakisa kan shugabanci, tatsar kudi daga mambobin jam’iyyar, da kuma sabawa ka’idoji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar FRSC ta bayyana dalilan yawan afkuwar hadura a titunan Nijeriya

Hukumar kiyaye afkuwar hadura ta Nijeriya FRSC ta bayyana cewa a mafiya yawan lokuta rashin hakuri, gudun wuce sa'a tare da karya dokokin hanya ne...

Abin murna ne yadda al’ummar Katsina suka tarbi Kashim Shettima – Gwamna Radda

Gwamnan Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya gode wa al’ummar jihar bisa irin tarbar da suka yi wa mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima, yayin ziyarar...

Mafi Shahara