DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar ADC a Kaduna ta kori mataimakin shugabanta da wasu ‘ya’yanta 8

-

Jam’iyyar hadaka ta ADC mai hamayya a Nijeriya reshen Kaduna ta kori mataimakin shugabanta na jihar tare da wasu manyan jami’anta guda takwas, bayan samun su da aikata laifukan da suka saba wa dokokinta.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa yayin wani taron manema labarai a Kaduna, shugaban jam’iyyar na jihar Elder Patrick Ambut, ya ce korar mutanen ya zama wajibi ne kasancewar ba za ta lamunci duk abin da zai kawo hargitsi ko zubar mata da kima ba.

Google search engine

Jam’iyyar ta zargi wadanda ta kora da aikata laifukan gudanar ta tarukan sirri don shirya manakisa kan shugabanci, tatsar kudi daga mambobin jam’iyyar, da kuma sabawa ka’idoji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara