DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba ni ke tsoma baki a gwamnatin Kano ko raba kwangiloli ba – Rabi’u Musa Kwankwaso

-

Jagoran jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya karyata zargin da ake yi masa na tsoma baki a harkokin mulkin Jihar Kano ko raba kwangiloli.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a wata hira da BBC Hausa, inda ya ce waɗannan zarge-zargen ba su da tushe, kuma ba ya ganin buƙatar ya mayar da martani ga masu adawa da shi.

Google search engine

Madugun darikar Kwankwasiyyar ya kara da cewa, gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf shi ne ke tafiyar da mulkinsa gaba ɗaya, kuma shi ne aka zaɓa da cikakken nazari tun bayan zaɓen 2019 kuma yanzu yana aiki cikin gaskiya da natsuwa, mu kuma mun ba shi dama ya yi aikinsa.

Tsohon gwamnan ya kuma musanta zancen cewa akwai rikici a jam’iyyar NNPP, yana mai cewa masu yada irin wannan magana ba ‘yan siyasa na gaskiya ba ne kamar yadda jaridar Daily Trust ta wallafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sabon shugaban hukumar zaben ya yi alwashin dawo da ingantacce da sahihin zabe a Nijeriya

Sabon shugaban hukumar zaɓen Nijeriya, INEC, Farfesa Joash Amupitan, SAN, ya sha alwashin dawo da sahihanci da amincewar jama’a ga tsarin zaɓe na ƙasar, yana...

Wani matashi ya yi ajalin abokinsa a jihar Kwara saboda budurwa

Wani matashi mai shekaru 25 da haihuwa mai suna Hammed Tunde, ya rasa ransa bayan abokinsa mai suna Gafar ya yi ajalin abokinsa da wuka...

Mafi Shahara