DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya za ta binciki bashin Dala miliyan 460 da aka karbo daga China lokacin mulkin Jonathan domin sanya CCTV a Abuja

-

Majalisar Wakilan Nijeriya ta amince da gudanar da bincike kan rancen dala miliyan 460 da gwamnatin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ta karɓa daga kasar China domin saka na’urorin CCTV an Abuja.

Wannan na zuwa ne bayan kudiri na gaggawa da dan majalisa Amobi Ogah, mai wakiltar mazabar Isuikwuato/Umunneochi ta jihar Abia ya gabatar a zaman majalisar na ranar Laraba.

Google search engine

Dan majalisar ya bayyana cewa an karɓi bashin ne tun shekarar 2010 domin sanya na’urorin tsaro a manyan wurare na Abuja, amma har yanzu aikin bai kammalu ba duk da cewa ana biyan bashin rancen.

Ogah ya kara da cewa, lamarin na da muhimmanci a sake dubawa ganin yadda matsalar tsaro ke ƙaruwa a birnin Abuja.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, a baya, majalisar ta 9 ta 2019 ta tambayi ma’aikatar kudi kan matsayin aikin, inda tsohuwar ministar kudi Zainab Ahmed ta tabbatar ana biyan bashin amma ba ta bayyana yadda aka kashe kuɗin ba.

Hakazalika, binciken zai taimaka wajen gano inda kudaden suka tafi da kuma dalilin da yasa aikin bai aiwatu ba duk da rancen da aka karɓa shekaru fiye da 10.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara