DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wani matashi ya yi ajalin abokinsa a jihar Kwara saboda budurwa

-

Wani matashi mai shekaru 25 da haihuwa mai suna Hammed Tunde, ya rasa ransa bayan abokinsa mai suna Gafar ya yi ajalin abokinsa da wuka a kirji sakamakon gardama da suka yi kan wata budurwa a unguwar Oja Gboro, cikin birnin Ilori, jihar Kwara.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata yayin da su biyun ke sayen rake a wajen wani mai sayarwa inda wani shaidu suka ce gardamar da ta fara da barkwanci ta rikide zuwa fada, inda Gafar, wanda ke da shekaru 21, ya fitar da wuka ya yi ajalin abokinsa.

Google search engine

Marigayin wanda ke zaune a Ile-Soro 2, Oja Gboro, an garzaya da shi zuwa wani asibiti mai zaman kansa, amma daga bisani aka tura shi asibitin gwamnati na Ilorin, inda likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.

Gafar kuma, wanda asalin dan Ile Olowo ne a yankin, ya tsere daga wajen bayan aikata laifin, kuma har yanzu ba a same shi ko ‘yan uwansa ba kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda ta jihar Kwara, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa kwamishinan ‘yan sanda, CP Adekimi Ojo, ya umurci da gudanar da cikakken bincike tare da tabbatar da an cafke wanda ake zargi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara