DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ka fito ka bayyana wa ‘yan Nijeriya hakikanin dalilin da ya sa ka canza hafsoshin tsaro – Bukatar ADC ga shugaba Tinubu

-

Jam’iyyar ADC ta bukaci shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya bayyana gaskiya ga ’yan Nijeriya kan ainihin dalilan da suka sa aka yi gaggawar sauya shugabannin rundunonin tsaron Nijeriya.

A wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Mallam Bolaji Abdullahi ya fitar, ADC ta bayyana damuwa kan yadda aka yi wannan canji a daidai lokacin da ake ta rade-radin yunƙurin juyin mulki a ƙasar.

Google search engine

Abdullahi ya ce kodayake Shugaban Ƙasa na da ikon yin irin waɗannan canje-canje, amma abin damuwa ne ganin cewa mafi yawan hafsoshin da aka cire sun shafe watanni 28 kacal a mukamansu, ciki har da shugaban rundunar tsaro wanda aka naɗa a matsayin shugaban sojojin ƙasa shekara ɗaya da ta wuce.

Bolaji ya ƙara da cewa, irin wannan mataki yana da tasiri mai zurfi ga zaman lafiyar rundunonin tsaro, don haka bai kamata a ɗauke shi ba tare da hujja mai ƙarfi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsare-tsaren Tinubu na farfaɗo da martabar Nijeriya a duniya -Kashim Shatima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce gyare-gyaren da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na sake gina martabar Nijeriya a idon duniya tare...

Gwamnatin Nijeriya na shirin dakatar da shigo da kayan tsaro daga waje

Gwamnatin Nijeriya ta yi niyyar kera dukkan makami da ake buƙata a cikin gida nan da shekara biyu zuwa biyar masu zuwa. Minista a ma'aikatar Tsaron...

Mafi Shahara