DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar Wakilai ta fara duba kudirin gyaran dokar EFCC domin ba ta cikakken ‘yanci

-

Majalisar wakilan Nijeriya ta karanta kudirin doka karo na biyu da ke neman gyara dokar kafa EFCC ta 2004 domin ba wa hukumar cikakken ‘yancin aiki ba tare da tsoma bakin siyasa ba.

Kudirin da ɗan majalisa daga jihar Filato, Yusuf Gagdi ya gabatar, ya ce gyaran zai sabunta tsarin hukumar da ya tsufa tun 2004.

Google search engine

Gagdi ya bayyana cewa laifukan kudi sun ƙaru da sababbin dabaru kamar safarar kudi ta yanar gizo da amfani da kudaden kirifto, sannan kuma dokar ba ta ba da kariya daga tsoma bakin siyasa.

Sabon kudirin na neman a rage ikon shugaban ƙasa wajen sauke shugaban EFCC, inda dole ne a samu amincewar kaso biyu bisa uku na majalisa kafin cire shi.

Gagdi ya kara da cewa, wannan gyaran zai tabbatar da sahihanci da ‘yancin hukumar, ƙarfafa amincewar jama’a, da karfafa yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rashin tabbas da matsalolin tsaro na barazana ga burin ECOWAS na 2050 – Shugaban ECOWAS, Touray

Shugaban kungiyar ECOWAS, Omar Touray, ya ce rashin tabbas a duniya, matsalolin tsaro da matsin tattalin arziki na hana kungiyar cimma burinta na Vision 2050,...

An yi ajalin wata mace mai juna biyu da wani karamin yaro a cikin birnin Kano

Al’ummar Sheka Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kano Municipal sun shiga firgici a daren Asabar bayan wasu da ba a san ko su waye ba...

Mafi Shahara