DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wike ya caccaki gwamnonin PDP saboda ware shi daga muhimman shawarwarin jam’iyya

-

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya soki gwamnonin jam’iyyar PDP bisa ware shi daga muhimman al’amuran jam’iyyar, yana gargadin cewa irin wannan dabi’a na iya rusa jam’iyyar.

Wike ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai a Abuja ranar Juma’a, inda ya nuna rashin jin daɗinsa saboda rashin gayyatarsa cikin tattaunawa kan manyan shawarwari, duk da irin rawar da ya taka a jam’iyyar tsawon shekaru.

Google search engine

Ya tambayi dalilin da yasa ake watsi da shi saboda kawai ba shi da kujerar gwamna, yana mai cewa matsayin sa na minista da kuma gudunmawar da ya bayar a baya sun isa ya ci gaba da kasancewa cikin tattaunawar jam’iyyar.

Hakazalika, ya kuma zargi wasu gwamnonin PDP da son mulki da yanke hukunci ba tare da shawara ba, yana mai cewa matsalolin jam’iyyar ba laifin APC ba ne, illa sakamakon rashin gaskiya da rashin bin tsarin da ke cikin jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara