Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya soki gwamnonin jam’iyyar PDP bisa ware shi daga muhimman al’amuran jam’iyyar, yana gargadin cewa irin wannan dabi’a na iya rusa jam’iyyar.
Wike ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai a Abuja ranar Juma’a, inda ya nuna rashin jin daɗinsa saboda rashin gayyatarsa cikin tattaunawa kan manyan shawarwari, duk da irin rawar da ya taka a jam’iyyar tsawon shekaru.
Ya tambayi dalilin da yasa ake watsi da shi saboda kawai ba shi da kujerar gwamna, yana mai cewa matsayin sa na minista da kuma gudunmawar da ya bayar a baya sun isa ya ci gaba da kasancewa cikin tattaunawar jam’iyyar.
Hakazalika, ya kuma zargi wasu gwamnonin PDP da son mulki da yanke hukunci ba tare da shawara ba, yana mai cewa matsalolin jam’iyyar ba laifin APC ba ne, illa sakamakon rashin gaskiya da rashin bin tsarin da ke cikin jam’iyyar.



