DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar NEMA ta karbi ‘yan Nijeriya 150 da suka makale a Nijar

-

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta bayyana karbar ‘yan kasar 150 da suka makale a kasar Nijar.

Bayanin na kunshe ne cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X, inda ta ce ‘yan Nijeriyar sun sauka a filin jirgin sama na Aminu Kano, da ke jihar Kano.

Google search engine

Labari mai alaka: Hukumar NEMA ta karbi ‘yan Nijeriya 147 da suka makale a Libya

Jaridar Punch ta ruwaito cewa wannan mataki yana cikin shirin mayar da mutane ainahin kasashensu, hadin gwiwa da gwamnati tare da majalisar dinkin duniya.

Hukumar NEMA ta ce cikin wadanda aka dawo da su akwai maza 88 da mata 32, sai kuma yara maza 14 da yara mata 16.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara