DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dokokin Nijeriya na shirin kirkirar sabbin jihohi da kananan hukumomi a fadin kasar

-

Majalisar dokokin tarayyar Nijeriya ta fara tattauna yiwuwar kirkirar sabbin jihohi 55 da kananan hukumomi 278 a fadin kasar.

 

Google search engine

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da hadimin mataimakin shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Isma’il Mudashir ya fitar, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

 

Sanarwar ta ce tattaunawar wani bangare ne na shirin yi wa kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999 kwaskwarima.

 

Ta kuma kara da cewa Sanata Barau I Jibrin, wanda ke jagorantar kwamitin majalisar dattawan kan gyaran kundin tsarin mulki, ya bukaci sauran ‘yan majalisar dokokin da su mayar da hankali wajen kammala yin kwaskwarimar kafin karshen shekarar 2025.

Labari mai alaka: Gwamnan Bauchi ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar

 

Ya bayyana cewa a daidai wannan gaba, akwai kudurori 69 da suka gabatar, bukatar kirkirar sabbin jihohi 55 da kananan hukumomi 278, baya ga yin gyara a iyakokin kasar guda biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara