DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matatar Dangote za ta ƙara yawan man da take tacewa zuwa ganga miliyan 1.4 a rana

-

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da shirin ƙara yawan samar da man da take tacewa daga ganga 650,000 zuwa ganga miliyan 1.4 a kowace rana, wanda idan an kammala zai zama mafi girma a duniya, ya zarce Jamnagar Refinery da ke Indiya.

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ne ya bayyana haka yayin taron manema labarai a Legas a ranar Lahadi, inda ya ce wannan mataki yana nuna aminci ga makomar Najeriya tare da daidaita da manufar Shugaba Bola Tinubu ta ganin kasar ta zama kan gaba a samar da man da aka tace a duniya.

Google search engine

Ya bayyana cewa wadannan manufofi sun sake fasalin sashen man fetur a ƙasa tare da karfafa zuba jari daga kamfanoni a harkar tace mai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara