DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar zabe za ta hada kai da majalisar wakilan Nijeriya domin gudanar da sahihin zabe

-

Shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya bayyana aniyarsa ta yin aiki tare da Majalisar Dokoki domin tabbatar da gudanar da sahihin zabe, adalci da gaskiya a Nijeriya.

Hakan na kunshe a cikin wata sanarwa da hukumar INEC ta fitar a ranar Litinin, inda Amupitan ya bayyana cewa hukumar INEC za ta yi aiki kafada da kafada da ‘yan majalisa wajen sake duba dokar zabe domin tabbatar da cewa sabbin gyare-gyare za su ɗauki darussa daga zabubbukan da aka yi a baya, tare da ƙara gina amincewar al’ummar Nijeriya ga hukumar zabe.

Google search engine

Ya ce manufar wannan gyara ita ce rage yawan ƙorafe-ƙorafen zabe ta hanyar tabbatar da gaskiya da adalci a kowane mataki na zabe ga kowane bangare.

Ya kara da cewa, doka ce ginshiƙin tabbatar da dimokuraɗiyya, don haka dole ne ayi abinda zai hana rikice-rikicen sakamakon zabe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun raba Naira biliyan 116.4 ga ɗalibai sama da dubu 624 – Asusun NELFUND

Asusun ba da bashin karatu ga ɗaliban manyan makarantu ya bayyana cewa ya raba Naira biliyan 116.4 ga ɗalibai sama da dubu 624, tun bayan...

Tsohon kwamishinan Ganduje ya soki gwamnatin Abba bisa zargin sayar da filin makarantar

Tsohon kwamishinan ilimi na a zamanin Ganduje, Muhammad Sanusi Sa'id Kiru, ya soki matakin gwamnatin Abba Kabir Yusuf na mayar da Makarantar Sakandare ta ‘Yan...

Mafi Shahara