DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar APC ta kalubalanci Gwamnan Filato Mutfwang da ya bayyana masu matsa masa lamba ya bar PDP

-

Jam’iyyar APC ta jihar Filato ta kalubalanci Gwamna Caleb Mutfwang da ya fito fili ya bayyana sunayen mutanen da ke matsa masa lamba ya bar jam’iyyar PDP ya koma APC.

Gwamnan ya bayyana a wani taro a fadar gwamnati da ke Jos cewa wasu jiga-jigan APC sun roƙe shi da ya shiga jam’iyyarsu, amma ya ce sai idan Allah da kuma jama’ar jihar sun yarda zai iya yanke wannan shawarar.

Google search engine

Sai dai mai magana da yawun jam’iyyar APC na riko a jihar, Shittu Bamaiyi, ya musanta ikirarin gwamnan, yana mai cewa wannan magana tana nuni ne da yadda gwamnatin Mutfwang ta gaza cika alkawuran da ta dauka ga al’umma,inda ya ce idan gaskiyane ya fito ya faɗi sunayen waɗanda ke matsa masa lamba, ya kuma bayyana su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun raba Naira biliyan 116.4 ga ɗalibai sama da dubu 624 – Asusun NELFUND

Asusun ba da bashin karatu ga ɗaliban manyan makarantu ya bayyana cewa ya raba Naira biliyan 116.4 ga ɗalibai sama da dubu 624, tun bayan...

Tsohon kwamishinan Ganduje ya soki gwamnatin Abba bisa zargin sayar da filin makarantar

Tsohon kwamishinan ilimi na a zamanin Ganduje, Muhammad Sanusi Sa'id Kiru, ya soki matakin gwamnatin Abba Kabir Yusuf na mayar da Makarantar Sakandare ta ‘Yan...

Mafi Shahara