DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna karɓar saƙonnin barazanar kawo mana hari a majalisa – Shugaban kwamitin tsaron majalisar waƙilai

-

Shugaban kwamitin tsaron cikin gida na Majalisar Wakilai, Honarabul Garba Ibrahim Muhammad, ya bayyana cewa majalisar na shan barazanar kai mata hari daga ’yan ta’adda, abin da ya haifar da bukatar karfafa tsaro a cikin ginin majalisar.

Honarabul Muhammad ya bayyana hakan ne a yayin jin ra’ayi kan kudirin kafa hukumar tsaron majalisa da aka gudanar a Abuja, inda ya ce majalisar ta zama abin bibiya ga miyagu da ke amfani da raunanan matakan tsaro.

Google search engine

A cewarsa sun sha barazana daga ’yan ta’adda da ke cewa zasu tarwatsa ginin majalisar, haka kuma wasu masu zanga-zanga sun yi barazanar rufe ta.

Ya ce kudirin yana nufin samar da tsaron da ya dace da abin da ake amfani da shi a majalisun kasashe masu ci gaba, domin kare ’yan majalisa, ma’aikata, da duk masu ziyartar ginin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tinubu ya cire masu manyan laifuka daga jerin wadanda za su amfana da afuwar shugaban kasa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan takardun afuwa da sassauta hukunci ga wasu mutane da aka taɓa yanke wa hukunci, domin aiwatar...

Sama da mutum 170 ne ke son zama ’yan Nijeriya daga kasashen ketare – Ministan cikin gida

Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji Ojo, ya bayyana cewa sama da ’yan kasashen ketare 170 ne suke neman zama ’yan Nijeriya. Tunji Ojo ya sanar da...

Mafi Shahara