DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna karɓar saƙonnin barazanar kawo mana hari a majalisa – Shugaban kwamitin tsaron majalisar waƙilai

-

Shugaban kwamitin tsaron cikin gida na Majalisar Wakilai, Honarabul Garba Ibrahim Muhammad, ya bayyana cewa majalisar na shan barazanar kai mata hari daga ’yan ta’adda, abin da ya haifar da bukatar karfafa tsaro a cikin ginin majalisar.

Honarabul Muhammad ya bayyana hakan ne a yayin jin ra’ayi kan kudirin kafa hukumar tsaron majalisa da aka gudanar a Abuja, inda ya ce majalisar ta zama abin bibiya ga miyagu da ke amfani da raunanan matakan tsaro.

Google search engine

A cewarsa sun sha barazana daga ’yan ta’adda da ke cewa zasu tarwatsa ginin majalisar, haka kuma wasu masu zanga-zanga sun yi barazanar rufe ta.

Ya ce kudirin yana nufin samar da tsaron da ya dace da abin da ake amfani da shi a majalisun kasashe masu ci gaba, domin kare ’yan majalisa, ma’aikata, da duk masu ziyartar ginin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in...

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025...

Mafi Shahara