Wannan umurni na Tinubu ya fito ne a cikin wata wasika da aka aika wa hukumar tattara haraji ta kasa FIRS da hukumar kula da albarkatun man fetur ta NMDPRA, wadda mai taimaka masa na musamman, Damilotun Aderemi, ya sanya wa hannu a ranar 21 ga Oktoba 2025.
Shugaban FIRS, Zacch Adedeji, ne ya gabatar da wannan shawarwarin ga shugaban ƙasa, inda ya bayyana cewa harajin zai taimaka wajen karfafa masana’antun tace mai, tabbatar da daidaiton farashin mai, da kuma kare darajar Naira a kasuwar mai.
Adedeji ya bayyana cewa rashin daidaito tsakanin farashin man da ake tacewa a gida da wanda ake shigowa da shi daga waje yana janyo tashin farashi a kasuwa.



