DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sulhu da ‘yan bindiga ba tare da an karbe makamansu ba, hatsari ne mai girma – Gwamna Dauda

-

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gargadi gwamnoni da hukumomin tsaro da su guji sulhu da ‘yan ta’adda da ba tare da an karɓe makamansu ba.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sulaiman idris ya fitar Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wani jawabi da ya gabatar a cibiyar nazarin tsaro ta kasa NISS da ke Abuja a ranar Laraba.

Google search engine

Gwamnan ya ce, yaki da ‘yan bindiga a Zamfara ya samo asali ne daga matsalolin tattalin arziki, rashin aikin yi, rikice-rikice da yaduwar makamai daga kasashen makwabta.

Gwamna Lawal ya jaddada cewa tatttaunawa da ‘yan ta’adda ba tare da an kwace makamansu ba ba dai-dai bane,zaman lafiya yana samuwa ne idan aka yi afuwa tare da karɓe makamansu,domin idan aka barsu da bindigu rikici ba zai kare ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yadda fitinar bayan zabe ta yi ajalin mutane sama da 700 a Tanzaniya

Jam’iyyar adawa ta Chadema a Tanzaniya ta bayyana cewa fiye da mutane 700 ne suka mutu cikin kwana uku na zanga-zangar bayan zaɓen shugaban ƙasa,...

Tinubu ya umurci sabbin hafsoshin tsaro da su murƙushe duk wata barazanar tsaro

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umurci sabbin hafsoshin tsaron da su tashi tsaye wajen murƙushe duk wata barazanar tsaro da ke tasowa a sassan...

Mafi Shahara