Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umurci sabbin hafsoshin tsaron da su tashi tsaye wajen murƙushe duk wata barazanar tsaro da ke tasowa a sassan Nijeriya.
Da yake bayani bayan tattabatar dasu a fadarsa a Alhamis dinnan, Tinubu ya ce barazanar tsaro na ta karuwa, kuma abin damuwa shi ne fitowar sabbin kungiyoyin ‘yan ta’adda a yankunan Arewa ta tsakiya, Arewa maso yamma da kuma wasu sassa na Kudu.
Ya ƙara da cewa ‘yan Nijeriya na bukatar zaman lafiya cikin gaggawa, don haka ya bukaci hafsoshin su yi aiki da kishin ƙasa.



