DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matatar man Dangote ta yi alkawarin samar da wadataccen man fetur a lokacin bukukuwan karshen shekara

-

Matatar man Dangote ta tabbatar da cewa za ta samar da isasshen man fetur da dizal a fadin Nijeriya a lokacin bukukuwan karshen shekara domin a cewar kamfanin, yawan man da ake tacewa a kullum yanzu ya haura abin da ake bukata.

Mai kula da harkokin yada labarai da dabarun kasuwanci na rukunin kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da aka samu daga ofishinsa a ranar Asabar, inda ya ce matatar tana fitar da lita miliyan 45 na fetur da lita miliyan 25 na dizal a kullum.

Google search engine

Chiejina, ya ce kamfanin na aiki tare da hukumomi da masu rarraba man domin tabbatar da isar sa cikin sauki a fadin kasar.

A cewarsa, karuwar tace man a cikin gida na taimakawa wajen karfafa Naira ta hanyar rage kudaden da ake fitarwa waje da kuma karfafa kudaden da ke shigowa cikin gida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da ake zargin Manjo Al Mustapha da hannu wajen halaka matar Abiola

Kotun Kolin Nijeriya ta yi watsi da shari’ar da aka shigar da Manjo Hamza Al Mustapha, kan zarginsa da hannu wajen halaka Kudirat Abiola, matar...

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen shekarar 2026 don gudanar da zaɓe a ƙasar

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

Mafi Shahara