DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matsalar Nijeriya ba ta addini ba ce illa rashin shugabanci nagari – Sowore

-

Dan gwagwarmayar kare hakkin dan’Adam kuma tsohon dan takarar shugaban kasa, Omoyele Sowore, ya mayar da martani ga kalaman shugaban Amurka, Donald Trump da ya bayyana cewa Kiristoci na fuskantar barazana a Nijeriya.

A wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, Sowore ya ce ceto Nijeriya ba zai fito daga waje ba, sai dai daga ingantaccen shugabanci a cikin gida. Sannan matsalar Nijeriya ba ta takaita ga addini ba, illa sakacin gwamnati, cin hanci, da rashin shugabanci mai nagarta.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito Sowore ya kara da cewa duka Kiristoci da Musulmai na fama da hare-haren ‘yan bindiga da talauci a sassa daban-daban na kasar, maimakon a rika kallon matsalolin tsaro ta fuskar addini, lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya za su hada kai wajen neman shugabanci nagari da kare rayukan jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara