DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matsalar Nijeriya ba ta addini ba ce illa rashin shugabanci nagari – Sowore

-

Dan gwagwarmayar kare hakkin dan’Adam kuma tsohon dan takarar shugaban kasa, Omoyele Sowore, ya mayar da martani ga kalaman shugaban Amurka, Donald Trump da ya bayyana cewa Kiristoci na fuskantar barazana a Nijeriya.

A wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, Sowore ya ce ceto Nijeriya ba zai fito daga waje ba, sai dai daga ingantaccen shugabanci a cikin gida. Sannan matsalar Nijeriya ba ta takaita ga addini ba, illa sakacin gwamnati, cin hanci, da rashin shugabanci mai nagarta.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito Sowore ya kara da cewa duka Kiristoci da Musulmai na fama da hare-haren ‘yan bindiga da talauci a sassa daban-daban na kasar, maimakon a rika kallon matsalolin tsaro ta fuskar addini, lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya za su hada kai wajen neman shugabanci nagari da kare rayukan jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da ake zargin Manjo Al Mustapha da hannu wajen halaka matar Abiola

Kotun Kolin Nijeriya ta yi watsi da shari’ar da aka shigar da Manjo Hamza Al Mustapha, kan zarginsa da hannu wajen halaka Kudirat Abiola, matar...

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen shekarar 2026 don gudanar da zaɓe a ƙasar

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

Mafi Shahara