‘Yan jaridu hudu ne da suka hada da shugaban gidan rediyo da talabijin sarauniya, kuma wakilin sashen Faransanci na RFI, Moussa Kaka hukumomin Nijar suka kama a ranar Lahadi 2 ga watan Nuwamba 2025.
Sauran ‘yan jaridar sun hada da editan sarauniyar, Ibro Chaibou da kuma wasu fitattun ‘yan jarida na Nijar irin su Souleymane Brah, da Oumarou Kane, da Seriba Yousouf
Daman a ranar 30 ga watan Oktoban da ya gabata ne aka kama shugaban kafar yada labaran ta Saurauniya kafin daga bisani a sake shi.



