DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu na amfani da karfi ga ‘yan adawa domin sauya sheka zuwa APC, in ji jam’iyyun adawa a Nijeriya

-

Wasu jam’iyyun adawa a Nijeriya na zargin Shugaba Bola Tinubu da amfani da kudaden gwamnati da hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa domin tilasta wa ‘yan adawa su koma jam’iyyar APC.

A cewar kakakin jam’iyyun PDP, NNPP da CUPP, wato Debo Ologunagba, Oladipo Johnson, da Mark Adebayo, sauya shekar da ake ta gani daga ‘yan adawa zuwa APC na nuna cewa jam’iyyar mai mulki na dab da rugujewa daga ciki.

Google search engine

Sai dai kakakin yaɗa labarai na APC, Bala Ibrahim, ya karyata zargin, yana mai cewa wadanda suka koma jam’iyyar sun yi hakan ne da son ransu saboda irin nasarorin da APC ke samu a mulki, kuma jam’iyyar na da cikakken tsari da zai hana ta fadawa rikicin cikin gida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna biyan ‘yan bindiga Naira miliyan 7 don zama a gidajenmu ko noma gonakinmu

Wasu al’ummomi a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja sun bayyana cewa suna biyan haraji ga ‘yan bindiga domin su samu damar zama a garuruwansu...

Abin takaici ne a ce tawagar Super Eagles na bin bashi – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023 Peter Obi, ya bayyana takaici kan rahotannin da ke nuna cewa tawagar wasan...

Mafi Shahara