DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akpabio ya musanta yin izgilanci ga Trump kan barazanar yaƙi da Nijeriya

-

Shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Godswill Akpabio, ya musanta wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke cewa ya yi izgilanci ga shugaban Amurka Donald Trump kan barazanar yaƙi da Nijeriya.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Eseme Eyiboh, ya fitar a Abuja ranar Litinin, Akpabio ya ce kalaman da aka danganta masa ƙarya ce kuma ƙoƙari ne na tayar da husuma tsakanin shi da shugaban Amurka.

Google search engine

A cewarsa, rubutun da wata kafar sada zumunta mai suna Rant HQ ta wallafa ba gaskiya ba ne, tare da zargin masu yada shi da neman haddasa rikici tsakanin Nijeriya da Amurka.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, sanarwar ta ƙara da cewa hoton da aka haɗa da rubutun an yi amfani da shi ne wajen ƙara wa ƙaryar armashi, domin ya sa jama’a su gaskata abin da bai furtawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ya bayyana masu digirin digirgir “Phd” 300 da Gidauniyar Kwankwasiyya ta samar a taronta na shekara-shekara

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma madugun Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya bayyana sama da masu digiri na uku (PhD) 300 da aka samar ta hanyar...

Gwamnatin Kano ta haramta biyan haraji da tsabar kudi daga 1 ga watan Janairu

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da cewa daga 1 ga Janairu, 2026, ba za a amince da biyan haraji da tsabar kuɗi ko takardar banki...

Mafi Shahara