DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akpabio ya musanta yin izgilanci ga Trump kan barazanar yaƙi da Nijeriya

-

Shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Godswill Akpabio, ya musanta wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke cewa ya yi izgilanci ga shugaban Amurka Donald Trump kan barazanar yaƙi da Nijeriya.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Eseme Eyiboh, ya fitar a Abuja ranar Litinin, Akpabio ya ce kalaman da aka danganta masa ƙarya ce kuma ƙoƙari ne na tayar da husuma tsakanin shi da shugaban Amurka.

Google search engine

A cewarsa, rubutun da wata kafar sada zumunta mai suna Rant HQ ta wallafa ba gaskiya ba ne, tare da zargin masu yada shi da neman haddasa rikici tsakanin Nijeriya da Amurka.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, sanarwar ta ƙara da cewa hoton da aka haɗa da rubutun an yi amfani da shi ne wajen ƙara wa ƙaryar armashi, domin ya sa jama’a su gaskata abin da bai furtawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara