DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An rantsar da shugabar kasar Tanzania, Samia Suluhu

-

Shugabar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan ta karbi rantsuwa a ranar Litinin bayan zaben da aka yi cikin tashin hankali kamar yadda rahotanni suka tabbatar.

Jam’iyyar adawa ta Chadema ta ce daruruwan mutane sun rasa rayukansu a hannun jami’an tsaro amma hukumar zabe ta bayyana cewa Suluhu ta lashe zaben da kashi 98 cikin dari.

Google search engine

An gudanar da bikin rantsuwar a fadar gwamnati da ke Dodoma ba tare da halartar jama’a ba, yayin da intanet ke a katse gaba ɗaya tun ranar zabe, wanda hakan ya hana samun sahihan bayanai daga kasar.

Wata majiyar diflomasiyya ta ce an samu rahotannin mutuwar mutane da dama a asibitoci, yayin da Chadema ta bayyana cewa sama da mutum 800 ne suka rasa rayukansu, duk da cewa babu tabbacin wannan adadi.

Hukumomin kasar sun musanta zargin amfani da karfin iko, yayin da makarantu da sufuri suka tsaya cak a fadin kasar kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yawan malaman kula da lafiya ‘yan Nijeriya da ke aiki a Ingila ya kai 16,00 – Rahoton Jaridar Punch

Akalla ma’aikatan jinya da ungozoma 16,156 ‘yan Nijeriya sun samu lasisin aiki a kasar Birtaniya tsakanin 2017 zuwa 30 ga Satumba, 2025, a cewar bayanan...

Cin hanci da rashawa na boye irin albarkar da Allah Ya ajiye a Nijeriya in ji shugaban hukumar EFCC

Shugaban Hukumar EFCC, Ola Olukoyede, ya ce cin hanci da rashawa na boye albarkar da Allah Ya yi wa Nijeriya tare da hana ƙasar cimma...

Mafi Shahara