DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba a take hakkin Kiristoci a Nijeriya ba – Babban hafsan tsaron Nijeriya

-

Babban hafsan tsaron Nijeriya Janar Olufemi Oluyede ya karyata ikirarin cewa ana zaluntar Kiristoci a Nijeriya, inda ya ce babbar matsalar Nijeriya ita ce ta’addanci.

Janar Oluyede ya bayyana hakan ne yayin zantawa da manema labarai a Abuja a ranar Litinin lokacin da ya mayar da martani kan kalaman shugaban Amurka Donald Trump wanda ya zargim ‘yan ta’adda na kai hare-hare kan Kiristoci.

Google search engine

Oluyede ya ce sojojin Nijeriya na aiki tuƙuru wajen yaƙar ta’addanci da tabbatar da tsaro, tare da samun nasara sakamakon sabon tsarin tsaro da shugaba Tinubu ya kafa.

Hakazalika ya ƙara da cewa rundunar soji za ta cigaba da ƙoƙari wajen dawo da zaman lafiya tare da buƙatar haɗin kan ƙasashen duniya domin yaƙi da ta’addanci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara