DCL Hausa Radio
Kaitsaye

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

-

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a yankin suna da alaka da halaka wasu mabiya addini, tana mai jaddada cewa ta’addanci yana shafar kowa ba tare da bambancin addini ko kabila ba.

A sanarwar da ta fitar a ranar Talata, ECOWAS ta bayyana cewa kungiyoyin ta’addanci na kai hare-hare a kasashe da dama ciki har da Nijeriya, inda ake hallaka fararen hula ba tare da bambanci ba.

Google search engine

Kungiyar ta yi kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran ƙasashe abokan hulɗa da su cigaba da tallafa wa kasashen yankin wajen yaki da tsattsauran ra’ayi da ta’addanci.

Sanarwar ta zo ne bayan shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana Nijeriya a matsayin “ƙasa mai damuwa ta musamman,” bisa zargin cewa ana barazana ga Kiristoci, abin da gwamnatin Nijeriyar ta musanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

Shugaba Tinubu ya nemi majalisa ta tabbatar da sabon minista daga jihar Enugu

Shugaba Bola Tinubu ya aika wa majalisar dattawan Nijeriya wasikar neman tantancewa da tabbatar da Dr. Kingsley Tochukwu Ude, babban lauya daga Jihar Enugu, a...

Mafi Shahara