DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kashim Shettima ya tafi Brazil domin halartar taron sauyin yanayi karo na 30

-

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bar Abuja zuwa Brazil domin wakiltar shugaba Bola Tinubu a babban taron sauyin yanayi na Majalisar Dinkin Duniya karo na 30 da za a gudanar a birnin Belém na kasar Brazil.

Taron, wanda shugaban Brazil, Luiz Inácio Lula da Silva ke jagoranta tare da hadin guiwar wasu kasashe, zai gudana daga ranar 6 zuwa 7 ga watan Nuwamba, inda za a tattauna batutuwan da suka shafi kariyar dazuka, halittu, da adalcin yanayi.

Google search engine

Mai magana da yawun ofishin mataimakin shugaban kasa, Stanley Nkwocha, ya bayyana cewa Shettima zai gabatar da jawabin Nijeriya kan sauyin yanayi, sannan ya halarci tarukan kwamitoci da za su tattauna batun canjin makamashi da yarjejeniyar Paris.

Haka kuma, Shettima zai yi ganawa da shugabanni da masu ruwa da tsaki don tattauna yadda Nijeriya za ta shiga kasuwar carbon finance da ake sa ran za ta samar da har dala biliyan uku a duk shekara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An fitar da jihohi 4 a Gasar Kokawar Nijar ta 2025

Kwana na uku da fara gasar kokawar gargajiya a Nijar tuni an yi waje da jihohi hudu daga cikin takwas na kasar daga jerin wanda...

Ya kamata a canza salon yadda ake yakar ‘yan bindiga a Nijeriya

Daga: Farfesa Usman Yusuf Litinin : 22 Disamba 2025 Ban taɓa gudu ko ja da baya ba ko nuna wata fargaba wajen bayyana matsayina a kan yaƙin...

Mafi Shahara