DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

-

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald Trump kan zargin kisan Kiristoci a kasar.

Trump ya yi wannan furuci ne bayan da Amurka ta sanya Nijeriya cikin jerin “kasashen da ke da damuwa ta musamman” saboda zargin wariyar addini, lamarin da ya jawo musayar yawu a tsakanin jakadun kasashen biyu.

Google search engine

Da yake jawabi a zauren majalisar a ranar Talata, shugaban majalisar dattawan Godswill Akpabio ya ce batun na da nasaba da manufofin diflomasiyya, don haka sai sun tuntubi gwamnatin tarayya kafin su dauki matsaya, sannan kuma kalaman Trump sun dogara ne da “tsohon rahoto na shekarar 2010” wanda bai yi daidai da halin da ake ciki a yanzu ba.

A cewarsa, matsalar tsaro a Nijeriya ba ta da alaka da addini, inda ya ce Musulmai da Kiristoci duka na fuskantar hare-hare iri daya daga ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara