DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya nemi majalisa ta tabbatar da sabon minista daga jihar Enugu

-

Shugaba Bola Tinubu ya aika wa majalisar dattawan Nijeriya wasikar neman tantancewa da tabbatar da Dr. Kingsley Tochukwu Ude, babban lauya daga Jihar Enugu, a matsayin sabon minista.

Shugaban majalisar dattawan, Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar a zaman da aka gudanar ranar Talata, inda ya mika sunan Ude ga kwamitin tantancewa don ci-gaba da nazari.

Google search engine

Nadin ya biyo bayan murabus din tsohon ministan kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, wanda ya ajiye aiki saboda rikicin takardun karatu da na yi wa kasa hidima wato NYSC.

Dr. Ude, wanda ke rike da mukamin kwamishinan shari’a na jihar Enugu, zai maye gurbin Nnaji a majalisar zartarwa ta Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara