DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya nemi majalisa ta tabbatar da sabon minista daga jihar Enugu

-

Shugaba Bola Tinubu ya aika wa majalisar dattawan Nijeriya wasikar neman tantancewa da tabbatar da Dr. Kingsley Tochukwu Ude, babban lauya daga Jihar Enugu, a matsayin sabon minista.

Shugaban majalisar dattawan, Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar a zaman da aka gudanar ranar Talata, inda ya mika sunan Ude ga kwamitin tantancewa don ci-gaba da nazari.

Google search engine

Nadin ya biyo bayan murabus din tsohon ministan kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, wanda ya ajiye aiki saboda rikicin takardun karatu da na yi wa kasa hidima wato NYSC.

Dr. Ude, wanda ke rike da mukamin kwamishinan shari’a na jihar Enugu, zai maye gurbin Nnaji a majalisar zartarwa ta Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara