DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ya kamata ka taka wa Matawalle burki – Jam’iyyar PDP ta shaida wa Tinubu

-

Kungiyar dattawan Arewa ta jam’iyyar PDP ta zargi ministan tsaron Nijeriya, Bello Matawalle, da jagorantar sauya shekar da dama daga PDP zuwa APC ta hanyar abin da ta kira cin hanci da tsoratarwa.

A wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na kasa, Dr Abbas Sadauki, ya fitar, ta ce, tsohon gwamnan na Zamfara yana amfani da mukaminsa da dukiyar da ya mallaka wajen jan magoya bayan PDP musamman a jihohin Zamfara da Kaduna su koma jam’iyyar APC.

Google search engine

Ƙungiyar ta ce matakin Matawalle wani yunkuri ne na raunana jam’iyyar PDP a yankin Arewa maso Yamma kafin zaɓen 2027, tana mai gargadin cewa, amfani da kuɗi da barazana wajen rusa jam’iyyar adawa na haifar da barazana ga dimokuraɗiyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan majalisar dokoki 6 a Jihar Zamfara sun fice daga PDP zuwa APC

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara 6 da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP sun sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, suna zargin take...

Kotu ta umurci hukumar EFCC ta gabatar da kwamshinan kudi na jihar Bauchi ga kotu bisa zargin safarar N4.6bn

Kotun Tarayya da ke Abuja ta umurci Hukumar EFCC da ta gabatar da Kwamishinan Kuɗin Jihar Bauchi, Yakubu Adamu, a ranar 30 ga Disamba domin...

Mafi Shahara