DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ya kamata ka taka wa Matawalle burki – Jam’iyyar PDP ta shaida wa Tinubu

-

Kungiyar dattawan Arewa ta jam’iyyar PDP ta zargi ministan tsaron Nijeriya, Bello Matawalle, da jagorantar sauya shekar da dama daga PDP zuwa APC ta hanyar abin da ta kira cin hanci da tsoratarwa.

A wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na kasa, Dr Abbas Sadauki, ya fitar, ta ce, tsohon gwamnan na Zamfara yana amfani da mukaminsa da dukiyar da ya mallaka wajen jan magoya bayan PDP musamman a jihohin Zamfara da Kaduna su koma jam’iyyar APC.

Google search engine

Ƙungiyar ta ce matakin Matawalle wani yunkuri ne na raunana jam’iyyar PDP a yankin Arewa maso Yamma kafin zaɓen 2027, tana mai gargadin cewa, amfani da kuɗi da barazana wajen rusa jam’iyyar adawa na haifar da barazana ga dimokuraɗiyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara