DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya nemi amincewar majalisa da ciyo bashin fiye da Naira tiriliyan daya

-

Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya nemi amincewar majalisar dattawa don karbo rancen Naira tiriliyan 1.15 daga kasuwar cikin gida domin cike gibin kasafin kuɗin shekarar 2025.

Wannan buƙata ta kasance cikin wasikar da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya karanta a zauren majalisa yayin zaman da aka gudanar a ranar Talata.

Google search engine

A cikin wasikar, Tinubu ya bayyana cewa rancen ya zama dole don samar da kuɗin da za a yi amfani da su wajen aiwatar da manyan shirye-shiryen gwamnati da ayyukan raya ƙasa.

A cewarsa, wannan tsari na rance wani ɓangare ne na dabarun gwamnati don farfaɗo da tattalin arziƙi, samar da ayyukan yi, da tabbatar da ci-gaban ƙasa.

Majalisar ta tura buƙatar zuwa kwamitin bashi na cikin gida da na ƙasashen waje domin yin nazari da bayar da rahoto cikin mako guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An fitar da jihohi 4 a Gasar Kokawar Nijar ta 2025

Kwana na uku da fara gasar kokawar gargajiya a Nijar tuni an yi waje da jihohi hudu daga cikin takwas na kasar daga jerin wanda...

Ya kamata a canza salon yadda ake yakar ‘yan bindiga a Nijeriya

Daga: Farfesa Usman Yusuf Litinin : 22 Disamba 2025 Ban taɓa gudu ko ja da baya ba ko nuna wata fargaba wajen bayyana matsayina a kan yaƙin...

Mafi Shahara