DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akpabio ya gargadi minista a majalisa da ka da ya amsa duk wata tambaya kan kalaman Trump

-

Shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Godswill Akpabio, ya gargadi wanda aka zaba domin mukamin minista, Barista Kingsley Udeh (SAN), da kada ya amsa kowace tambaya da ta shafi kalaman shugaban Amurka Donald Trump game da Nijeriya.

Udeh, wanda shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya zaba domin maye gurbin tsohon ministan kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, ya bayyana a gaban majalisar a ranar Alhamis don tantancewa.

Google search engine

Nnaji ya yi murabus ne a watan da ya gabata bayan cece-kuce kan sahihancin takardun karatunsa.

Lokacin tantancewar, Akpabio ya bukaci Udeh da ya gabatar da kansa sannan ya ce, tambayar da kawai zan roƙe ka kada ka amsa ita ce wadda ta shafi Trump.

Daga karshe, majalisar ta amince da nadin Udeh a matsayin minista ta hanyar kada kuri’ar murya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara