DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akwai yiwuwar madugun adawar Kamaru Isa Tchiroma yana Nijeriya ya boye – Rahotanni

-

Madugun adawar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, wanda ya kalubalanci nasarar Paul Biya, yana iya kasancewa yana a Nijeriya kamar yadda Africa Intelligence ta ce, amma wasu majiyoyi sun ce ya koma Abuja a ruwaitowar jaridar Daily Trust.

Rahoton ya ce an fitar da shi daga gidansa da ke Marouaré a Garoua tsakanin 28 da 29 ga watan Oktoba inda a sakonsa na Facebook, ya gode wa sojojin da suka raka shi zuwa wuri mai aminci.

Google search engine

A cewar rahoton, an tsallaka da shi zuwa Nijeriya bayan fargabar kai masa hari daga jami’an tsaro yayin da a safiyar 29 ga watan Oktoba, aka ji harbe-harbe a unguwarsa.

Ministan harkokin cikin gida, Paul Atanga Nji, ya gargade shi kan tada rikicin bayan zabe, yana mai cewa ya karya doka da ya ayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zabe kafin sakamakon hukuma ya fita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fusatattun matasa sun hallaka limamin masallaci a jihar Kwara bisa zargin maita

Wasu fusatattun matasa a garin Sokupkpan da ke ƙaramar hukumar Edu a jihar Kwara sun hallaka limamin masallacin yankin, Malam Abdullahi Audu, bisa zargin cewa...

Majalisar dokokin Amurka ta gabatar da kudirin hukunta jami’an gwamnatin Nijeriya

Majalisar dokoki ta Amurka ta gabatar da sabon kudiri mai taken “Nigeria Religious Freedom Accountability Act of 2025”, wadda ke neman hukunta jami’an gwamnatin Nijeriya...

Mafi Shahara