DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Baba-Ahmed ya bukaci Tinubu ya fito ya yi ma ‘yan Nijeriya bayani kan barazanar Amurka

-

Tsohon mai ba wa shugaban kasa shawara, Dr. Hakeem Baba-Ahmed, ya bukaci shugaba Bola Tinubu da ya fito fili ya yi wa ’yan Nijeriya jawabi kan barazanar mamayar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa ƙasar.

A wata sanarwa da ya wallafa a Facebook ranar Alhamis, Baba-Ahmed ya bayyana damuwa cewa shugaban kasa bai ce komai kai tsaye ba tun bayan da lamarin ya faru kuma wannan shiru na iya nuna rauni da rashin tsari a shugabanci.

Google search engine

A cewarsa, bai kamata ministoci ko kakakai su rika magana ba, sai shugaban kasa da kansa ya fito ya tabbatar da matsayin Nijeriya da matakan da gwamnati ke ɗauka.

Haka kuma ya gargadi Tinubu da kada ya yi niyyar tafiya Amurka don ganawa da Trump, yana mai cewa hakan zai kara bata sunan Nijeriya.

Baba-Ahmed ya bukaci shugaban kasa da ya dauki mataki cikin gaggawa ta hanyar nada jakadu, farfaɗo da hulɗar diflomasiyya, da yin jawabi kai tsaye ga ’yan ƙasa don tabbatar da cewa Nijeriya tana da murya da matsayin kanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sarakunan gargajiya ne kan gaba wajen samar da zaman lafiya – Kungiyar International Alert

Gudunmuwar da sarakunan gargajiya ke badawa wajen samar da zaman lafiya, ba abin yadawa ba ce - Kungiyar International Alert Ƙungiyar International Alert Nigeria ta bayyana...

Rundunar sojin saman Nijeriya ta yi alkawarin kare rayukan farar hula lokacin gudanar da ayyuka

Babban hafsan sojin saman Nijeriya, Air Marshal Sunday Aneke, ya ce rundunar sojin sama za ta mayar da hankali kan kare rayukan fararen hula da...

Mafi Shahara