DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dokokin Amurka ta gabatar da kudirin hukunta jami’an gwamnatin Nijeriya

-

Majalisar dokoki ta Amurka ta gabatar da sabon kudiri mai taken “Nigeria Religious Freedom Accountability Act of 2025”, wadda ke neman hukunta jami’an gwamnatin Nijeriya da ake zargin suna da hannu wajen take hakkin ’yancin addini da cin zarafin jama’a.

Kudirin, wanda dan majalisa Marlin Stutzman daga jihar Indiana ya dauki nauyinsa, an gabatar da shi ne a ranar 21 ga Oktoba, kuma yanzu yana gaban kwamitocin kula da harkokin wajen Amurka da na shari’a domin nazari.

Google search engine

A cikin kudirin, an umarci shugaban Amurka da ya sanya takunkumi ga jami’an Nijeriya da ke da hannu ko suka amince da cin zarafi na addini, ciki har da gwamnoni, alkalai, da jami’an tsaro da suka aiwatar da dokokin batanci ko suka rufe ido kan tashin hankali da aka yi da sunan addini.

Idan aka amince da kudirin, zai bai wa Amurka damar sanya takunkumi kan duk wani jami’i ko hukumomi a Nijeriya da ake zargin suna goyon bayan zalunci ko laifukan da suka saba wa ’yancin addini, abin da zai kara tsananta matsin lamba daga Washington kan Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara