DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar sojin saman Nijeriya ta yi alkawarin kare rayukan farar hula lokacin gudanar da ayyuka

-

Babban hafsan sojin saman Nijeriya, Air Marshal Sunday Aneke, ya ce rundunar sojin sama za ta mayar da hankali kan kare rayukan fararen hula da gujewa mummunan hari kan farar hula yayin ayyukanta.

Aneke ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis, yayin ganawarsa ta farko da manyan hafsoshin rundunar a hedikwatar rundunar da ke Abuja, inda ya ce wannan mataki na cikin abin da shugaban Bola Tinubu ke bukata daga dakarun kasa.

Google search engine

Aneke ya ce rundunar za ta karfafa hulɗa da al’umma da kuma hadin kai da sauran hukumomin tsaro domin murkushe ta’addanci da hana maƙiya samun mafaka, sannan kuma kare rayukan fararen hula da gujewa mummunan hari shi ne ginshikin kwarewar aikin.

Hakazalika, ya kuma tabbatar wa hafsoshin cewa dukkan matakan rundunar za su bi umarnin shugaban kasa kai tsaye, tare da mayar da hankali kan inganci, tsaro da kare martabar sojin sama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Akwai yiwuwar madugun adawar Kamaru Isa Tchiroma yana Nijeriya ya boye – Rahotanni

Madugun adawar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, wanda ya kalubalanci nasarar Paul Biya, yana iya kasancewa yana a Nijeriya kamar yadda Africa Intelligence ta ce, amma...

Fusatattun matasa sun hallaka limamin masallaci a jihar Kwara bisa zargin maita

Wasu fusatattun matasa a garin Sokupkpan da ke ƙaramar hukumar Edu a jihar Kwara sun hallaka limamin masallacin yankin, Malam Abdullahi Audu, bisa zargin cewa...

Mafi Shahara