DCL Hausa Radio
Kaitsaye

’Yan Majalisar Amurka 9 sun bukaci Amurka ta dauki mataki kan rikicin zaben Kamaru

-

Wasu ’yan majalisar dokokin Amurka tara sun rubuta wa sakataren harkokin wajen kasar, Marco Rubio, suna nuna damuwa kan tashin hankali, kisa, da kama mutane da dama da suka biyo bayan zaben shugaban kasa na Kamaru da aka gudanar a ranar 12 ga watan Oktoba.

A cikin wasikar, ’yan majalisar sun soki yadda gwamnati ke danniya kan masu zanga-zanga cikin lumana, tare da kira da a hukunta wadanda ke da hannu wajen kashe fararen hula. Sun bukaci gwamnatin Amurka ta matsa wa hukumomin Kamaru lamba domin su mutunta dimokuradiyya da hakkin dan Adam.

Google search engine

Wannan mataki ya biyo bayan yadda ake samun matsin lamba daga kasashen duniya, bayan rahotannin kashe mutane da dama da kama daruruwan mutane da kuma takurawa ’yan adawa bayan sake zaben shugaba Paul Biya da ake tantama a kai.

Masana harkokin diflomasiyya na ganin wannan matakin na ’yan majalisar Amurka a matsayin alamar cewa Washington na bin lamarin Kamaru da ido sosai kamar yadda jaridar MMI News ta wallafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara