DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Duk da tallafin kudaden tsaro daga Amurka, an kasa kare rayukan Kiristoci a Nijeriya – Dan majalisar Amurka

-

Ɗan majalisar Amurka Riley Moore ya zargi gwamnatin Nijeriya da gazawa wajen kare Kiristoci duk da biliyoyin dalolin tallafin tsaro da take samu daga Amurka.

Jaridar Punch ta ruwaito Moore, wanda ke jagorantar kwamitin binciken da shugaban Amurka Donald Trump ya kafa kan zargin gallaza wa Kiristoci a Nijeriya, ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da aka yi da shi a wani shiri na The Dinesh D’Souza a daren Alhamis.

Google search engine

Moore ya ce ‘yan’uwansa Kiristoci ana kashe su saboda imaninsu ga Yesu Almasihu, yana mai sukar shiru daga hukumomin Nijeriya da kuma kasashen duniya tare da gargadi cewa rashin daukar mataki kan matsalar na iya jawo tasirin tsaro mai muni.

Hakazalika, Moore ya bayyana halin da ake ciki a matsayin “kisan kiyashi da aka manta da shi”, inda ya bukaci Nijeriya da abokanta na waje da su dauki matakan gaggawa don kare rayukan Kiristoci da kawo karshen tashin hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara