DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Neja ya sallami shugaban hukumar SUBEB daga aiki

-

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya kori shugaban hukumar ilimin firamare ta Jiha (SUBEB), Muhammad Baba Ibrahim, tare da dukkan mambobin dindindin na hukumar.

Sanarwar ta fito ne daga sakataren gwamnatin jiha, Alhaji Abubakar Usman, a ranar Juma’a, inda ya ce matakin yana cikin kokarin gwamnati na sake fasalin tsarin ilimi domin inganta aiki da gaskiya a fannin ilimi.

Google search engine

A cewarsa, dukkan mambobin hukumar da sakataren su mika dukkan takardu, kadarori da ragamar aiki ga babban sakataren ma’aikatar ilimin firamare da sakandare ta jihar.

Gwamna Bago ya gode wa wadanda aka kora bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci-gaban ilimi a jihar, tare da yi musu fatan alheri a ayyukan da za su gabatar nan gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara