Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya kori shugaban hukumar ilimin firamare ta Jiha (SUBEB), Muhammad Baba Ibrahim, tare da dukkan mambobin dindindin na hukumar.
Sanarwar ta fito ne daga sakataren gwamnatin jiha, Alhaji Abubakar Usman, a ranar Juma’a, inda ya ce matakin yana cikin kokarin gwamnati na sake fasalin tsarin ilimi domin inganta aiki da gaskiya a fannin ilimi.
A cewarsa, dukkan mambobin hukumar da sakataren su mika dukkan takardu, kadarori da ragamar aiki ga babban sakataren ma’aikatar ilimin firamare da sakandare ta jihar.
Gwamna Bago ya gode wa wadanda aka kora bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci-gaban ilimi a jihar, tare da yi musu fatan alheri a ayyukan da za su gabatar nan gaba.



