DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Neja ya sallami shugaban hukumar SUBEB daga aiki

-

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya kori shugaban hukumar ilimin firamare ta Jiha (SUBEB), Muhammad Baba Ibrahim, tare da dukkan mambobin dindindin na hukumar.

Sanarwar ta fito ne daga sakataren gwamnatin jiha, Alhaji Abubakar Usman, a ranar Juma’a, inda ya ce matakin yana cikin kokarin gwamnati na sake fasalin tsarin ilimi domin inganta aiki da gaskiya a fannin ilimi.

Google search engine

A cewarsa, dukkan mambobin hukumar da sakataren su mika dukkan takardu, kadarori da ragamar aiki ga babban sakataren ma’aikatar ilimin firamare da sakandare ta jihar.

Gwamna Bago ya gode wa wadanda aka kora bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci-gaban ilimi a jihar, tare da yi musu fatan alheri a ayyukan da za su gabatar nan gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Arewa za su tattauna yadda za a shawo kan matsalar tsaro a yankin

An shirya gudanar da babban taron tsaro a Birnin Kebbi, babban birnin jihar Kebbi, a ranar Litinin, 10 ga Nuwamba, 2025, domin tattauna hanyoyin magance...

Shugaba kasar China Xi Jinping ya taya Paul Biya murnar nasarar zabe a Kamaru

Shugaban kasar China, Xi Jinping, ya taya shugaban Kamaru, Paul Biya, murnar sake lashe zaben shugabancin kasa, yana mai jaddada karfafa dangantaka mai karfi da...

Mafi Shahara