DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Manyan Arewa za su tattauna yadda za a shawo kan matsalar tsaro a yankin

-

An shirya gudanar da babban taron tsaro a Birnin Kebbi, babban birnin jihar Kebbi, a ranar Litinin, 10 ga Nuwamba, 2025, domin tattauna hanyoyin magance karuwar matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya.

Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III zai jagoranci taron tare da tsohon hafsan hafsoshin soji kuma tsohon ministan cikin gida, Laftanar Janar Abdulrahman Bello Dambazau (rtd), tare da halartar gwamnonin Arewa, masana tsaro da sauran manyan jami’ai.

Google search engine

Shugaban kungiyar Arewa Broadcast Media Practitioners Forum, Alhaji Yelwa, ya ce taron zai samar da dandalin tattaunawa da hadin kai domin dawo da zaman lafiya da karfafa hadin kan kasa.

A cewarsa, taron zai hada ‘yan jarida, masu tsara manufofi, jami’an tsaro da kungiyoyin ci-gaba domin tsara dabarun sadarwa da za su taimaka wajen gina yardar jama’a, hana tsattsauran ra’ayi da tallafa wa gyaran tsarin tsaro na Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan Neja ya sallami shugaban hukumar SUBEB daga aiki

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya kori shugaban hukumar ilimin firamare ta Jiha (SUBEB), Muhammad Baba Ibrahim, tare da dukkan mambobin dindindin na hukumar. Sanarwar...

Shugaba kasar China Xi Jinping ya taya Paul Biya murnar nasarar zabe a Kamaru

Shugaban kasar China, Xi Jinping, ya taya shugaban Kamaru, Paul Biya, murnar sake lashe zaben shugabancin kasa, yana mai jaddada karfafa dangantaka mai karfi da...

Mafi Shahara