DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NAPTIP ta ceto mutane 221 daga hannun masu fataucin mutane a jihar Jigawa

-

Hukumar da ke kula da hana fataucin mutane, NAPTIP ta jihar Jigawa ta ce ta ceto mutane 221 da aka yi fataucinsu cikin shekaru biyu da suka gabata.

Kwamandan hukumar a jihar, Malam Abdulladir Turajo, ya bayyana hakan a taron wayar da kai da aka gudanar a Kazaure, inda ya ce an maido da waɗanda aka ceto zuwa ga iyalansu tun bayan kafa ofishin hukumar a watan Yuli 2023.

Google search engine

A cewarsa, hukumar ta samu hukunta masu laifina sau biyu tare da gudanar da shirye-shiryen wayar da kai guda 175 a makarantu, kasuwanni, wuraren ibada da tashoshin mota a fadin jihar.

Taron wanda aka shirya tare da ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar Jigawa, na cikin shirin fadakarwa a matakin ƙananan hukumomi 27 na jihar, kuma an fara shi da yankin arewa maso yamma na jihar Jigawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Arewa za su tattauna yadda za a shawo kan matsalar tsaro a yankin

An shirya gudanar da babban taron tsaro a Birnin Kebbi, babban birnin jihar Kebbi, a ranar Litinin, 10 ga Nuwamba, 2025, domin tattauna hanyoyin magance...

Gwamnan Neja ya sallami shugaban hukumar SUBEB daga aiki

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya kori shugaban hukumar ilimin firamare ta Jiha (SUBEB), Muhammad Baba Ibrahim, tare da dukkan mambobin dindindin na hukumar. Sanarwar...

Mafi Shahara