DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NAPTIP ta ceto mutane 221 daga hannun masu fataucin mutane a jihar Jigawa

-

Hukumar da ke kula da hana fataucin mutane, NAPTIP ta jihar Jigawa ta ce ta ceto mutane 221 da aka yi fataucinsu cikin shekaru biyu da suka gabata.

Kwamandan hukumar a jihar, Malam Abdulladir Turajo, ya bayyana hakan a taron wayar da kai da aka gudanar a Kazaure, inda ya ce an maido da waɗanda aka ceto zuwa ga iyalansu tun bayan kafa ofishin hukumar a watan Yuli 2023.

Google search engine

A cewarsa, hukumar ta samu hukunta masu laifina sau biyu tare da gudanar da shirye-shiryen wayar da kai guda 175 a makarantu, kasuwanni, wuraren ibada da tashoshin mota a fadin jihar.

Taron wanda aka shirya tare da ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar Jigawa, na cikin shirin fadakarwa a matakin ƙananan hukumomi 27 na jihar, kuma an fara shi da yankin arewa maso yamma na jihar Jigawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara