DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba kasar China Xi Jinping ya taya Paul Biya murnar nasarar zabe a Kamaru

-

Shugaban kasar China, Xi Jinping, ya taya shugaban Kamaru, Paul Biya, murnar sake lashe zaben shugabancin kasa, yana mai jaddada karfafa dangantaka mai karfi da dadadden tarihi tsakanin kasashen biyu.

A cewar rahoton da ma’aikatar harkokin wajen kasar China ta wallafa a ranar Juma’a, Xi ya bayyana cewa kasashen biyu sun gina amincewar juna ta siyasa tare da cimma manyan nasarori a fannonin hadin gwiwa daban-daban a cikin ‘yan shekarun nan.

Google search engine

Xi ya kara da cewa kasar China za ta cigaba da inganta huldar diflomasiyya, tattalin arziki da al’adu da kasar Kamaru a kokarin da take yi na karfafa alaka da nahiyar Afirka.

Haka kuma, ya jaddada cewa kasashen biyu suna ci-gaba da marawa juna baya kan muhimman al’amura da bukatun da suka shafi kasashensu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Arewa za su tattauna yadda za a shawo kan matsalar tsaro a yankin

An shirya gudanar da babban taron tsaro a Birnin Kebbi, babban birnin jihar Kebbi, a ranar Litinin, 10 ga Nuwamba, 2025, domin tattauna hanyoyin magance...

Gwamnan Neja ya sallami shugaban hukumar SUBEB daga aiki

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya kori shugaban hukumar ilimin firamare ta Jiha (SUBEB), Muhammad Baba Ibrahim, tare da dukkan mambobin dindindin na hukumar. Sanarwar...

Mafi Shahara