DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba kasar China Xi Jinping ya taya Paul Biya murnar nasarar zabe a Kamaru

-

Shugaban kasar China, Xi Jinping, ya taya shugaban Kamaru, Paul Biya, murnar sake lashe zaben shugabancin kasa, yana mai jaddada karfafa dangantaka mai karfi da dadadden tarihi tsakanin kasashen biyu.

A cewar rahoton da ma’aikatar harkokin wajen kasar China ta wallafa a ranar Juma’a, Xi ya bayyana cewa kasashen biyu sun gina amincewar juna ta siyasa tare da cimma manyan nasarori a fannonin hadin gwiwa daban-daban a cikin ‘yan shekarun nan.

Google search engine

Xi ya kara da cewa kasar China za ta cigaba da inganta huldar diflomasiyya, tattalin arziki da al’adu da kasar Kamaru a kokarin da take yi na karfafa alaka da nahiyar Afirka.

Haka kuma, ya jaddada cewa kasashen biyu suna ci-gaba da marawa juna baya kan muhimman al’amura da bukatun da suka shafi kasashensu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara