Shugaban kasar China, Xi Jinping, ya taya shugaban Kamaru, Paul Biya, murnar sake lashe zaben shugabancin kasa, yana mai jaddada karfafa dangantaka mai karfi da dadadden tarihi tsakanin kasashen biyu.
A cewar rahoton da ma’aikatar harkokin wajen kasar China ta wallafa a ranar Juma’a, Xi ya bayyana cewa kasashen biyu sun gina amincewar juna ta siyasa tare da cimma manyan nasarori a fannonin hadin gwiwa daban-daban a cikin ‘yan shekarun nan.
Xi ya kara da cewa kasar China za ta cigaba da inganta huldar diflomasiyya, tattalin arziki da al’adu da kasar Kamaru a kokarin da take yi na karfafa alaka da nahiyar Afirka.
Haka kuma, ya jaddada cewa kasashen biyu suna ci-gaba da marawa juna baya kan muhimman al’amura da bukatun da suka shafi kasashensu.



