DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Miyetti Allah ta koka kan hare-haren da ake kai wa Fulani a jihar Benue

-

Kungiyar Miyetti Allah reshen Jihar Benue ta roki gwamnatin Nijeriya da ta jiha da su shiga tsakani kan abin da ta bayyana a matsayin hare-hare da ake ta kaiwa ‘ya’yanta a karamar hukumar Ohimini a jihar Benue.

Shugaban kungiyar na jiha, Ardo Muhammad, wanda ya sa hannu kan wata sanarwa a ranar Juma’a, ya zargi al’ummar Awule tare da jami’an sa-kai na jihar da kai hare-hare kan sansanonin Fulani a yankin.

Google search engine

Muhammad ya bayyana cewa rikicin ya fara ne a karshen watan Agusta 2025 lokacin da wasu ‘yan bindiga daga al’ummar Awule tare da taimakon jami’an sa-kai suka kai hari kan sansanonin Fulani, inda suka kona sansanoni shida, suka kashe shanu 30, suka sace wasu, tare da kashe wani makiyayi mai suna Isu Abdulkarim.

A cewarsa, hare-haren sun ci-gaba a makonnin baya-bayan nan, abin da ya janyo asarar dabbobi da kuma raba makiyaya da muhallansu, yana mai musanta rahotannin da ke cewa makiyaya sun kai farmaki kan manoma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara