DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban kasar Djibouti zai sake tsayawa takara karo na shida

-

Shugaban ƙasar Djibouti mai shekaru 77, Ismail Omar Guelleh zai sake tsayawa takara karo na shida

Shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh, wanda yake mulki tun daga 1999, zai sake tsayawa takara a karo na shida a zaɓen shugaban ƙasa da za a gudanar a shekara mai zuwa, bayan majalisar dokokin ƙasar ta cire dokar da ke hana wanda ya haura shekara 75 tsayawa takara.

Google search engine

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito cewa shugaban majalisar dokokin kasar, Dileita Mohamed Dileita, ne ya tabbatar da hakan bayan taron jam’iyyar RPP, inda ya ce sun gama amincewa da Guelleh a matsayin ɗan takara.

Guelleh, mai shekaru 77, ya kasance cikin jerin tsoffin shugabannin Afirka da ke neman tsawaita mulkinsu, irin su Paul Biya mai shekara 92 na Kamaru, da Alassane Ouattara mai shekara 83 na Côte d’Ivoire.

A zaɓen shekarar 2021 ya samu nasara da kaso 97 cikin ɗari, yayin da jam’iyyarsa ke da rinjaye a majalisar dokokin kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan takarar ADC a zaben gwamnan Anambara ya zargi jam’iyyar APGA da sayen kuri’u

Dan takarar ADC a zaben gwamnan Anambra, John Nwosu, ya zargi jam’iyyar APGA da sayan da kuri’a a zaben da yake ci-gaba da gudana a...

Ya kamata Nijeriya ta farka daga barcin da take yi saboda barazanar da Trump ya yi mata – Bishop Kukah

Shugaban Cocin Katolika a Sokoto Archbishop Matthew Kukah ya bayyana cewa barazanar Shugaban Amurka Donald Trump kan yiwuwar kai harin ga Nijeriya a matsayin nuni...

Mafi Shahara