DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata dattijuwa ta barke da kuka bayan an hanata kada kuri’a

-

Wata datijuwa mai shekaru 96 a duniya, Mrs. Elizabeth Onike, ta barke da kuka a rumfar zaɓe saboda an hana ta kada kuri’a a Anambara

Dattijuwar wadda ke zabe a akwatin Umudim Akasi Polling Unit 019, Agulu II, Ward 8, a ƙaramar hukumar Anaocha, jihar Anambra, a ranar Asabar.

Google search engine

Da take magana cikin harshen Igbo, tsohuwar ta bayyana takaicinta cewa a nan take yin zaɓe tun da dadewa.

Rahoton jaridar Punch ya ce ta ma kada kuri’a a zaɓen da ya gabata, amma yanzu jami’an INEC suna cewa katinta ba shi da inganci.

Elizabeth ta ji takaici matuka saboda ba za ta kada kuri’a a wannan zaɓen ba, wanda zai tantance wanda zai zama sabon gwamna ta.

Lamarin ya jawo tausayawa da damuwa daga wasu masu zaɓe da ke wajen, inda da dama suka yi kira ga hukumar INEC da ta duba irin waɗannan matsaloli domin kare haƙƙin zaɓen tsofaffi a nan gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ya kamata Nijeriya ta farka daga barcin da take yi saboda barazanar da Trump ya yi mata – Bishop Kukah

Shugaban Cocin Katolika a Sokoto Archbishop Matthew Kukah ya bayyana cewa barazanar Shugaban Amurka Donald Trump kan yiwuwar kai harin ga Nijeriya a matsayin nuni...

Lewandowski ba zai bar Barcelona a watan Junairu ba

Rahotanni na nuni da cewa Robert Lewandowski ba zai bar Barcelona a watan Janairu ba, amma akwai yiwuwar kashi 90 cikin 100 zai bar ƙungiyar...

Mafi Shahara