Shugaban Cocin Katolika a Sokoto Archbishop Matthew Kukah ya bayyana cewa barazanar Shugaban Amurka Donald Trump kan yiwuwar kai harin ga Nijeriya a matsayin nuni ga kasar da ta farka daga baccin da take yi.
Da yake jawabi a wajen bikin cika shekaru 60 da haihuwa na Dr. Reuben Abati a Legas, Bishop Kukah ya lokaci ya yi da Nijeriya za ta tashi daga dogon barcin da ke yi, ta sake ginuwa da gaskiya da kishin kasa.
A makon da ya gabata ne Shugaba Trump na Amurka ya yi ikirarin cewa ana cin zarafin Kiristoci a Nijeriya, yana kuma barazanar daukar matakan soja da ci-re tallafin da Amurka ke bai wa kasar.



